Isa ga babban shafi
Turkiya

Turkiya ta kame mutane 700 ma su son shiga IS

Kasar Turkiyya ta kori mutane sama da 700 a bana ‘yan kasashen waje da suka shiga kasar ko kuma neman tsallakawa zuwa Syria don taimakawa Mayakan IS da ke da’awar Jihadi.

Shugaban Kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan
Shugaban Kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan REUTERS/Harun Ukar
Talla

Cemalettin Hasimi mai Magana da yawun Firaministan Turkiya ya fadawa manema labarai a birnin Paris a kasar Faransa cewa a bara kawai ma su son shiga 520 aka kama, kuma daga shekara ta 2011 da aka fara yaki a Syria, Turkiya ta kama wadanda ke shirin tafiya Syria akalla 1,800.

Hasimi ya ce hatta ‘yan kungiyar Daesh da na PKK da ke kasar na da hatsari ga Turkiyya.

A cewarsa a kungiyar Daesh a Turkiya na da membobi a kasashe sama da 100, kuma suna ganin muddin aka ci gada da rikici a Syria zata fadada ayyukanta.
Hasimi ya ce suna e bukatar a yi sulhu a kasar Syria domin dakile barazanar ‘Yan ta’adda a Turkiya.

Ya ce Turkiyya na da sunayen ‘yan ta’adda dubu 16,000 da ta haramtawa tsoma kafar su a cikin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.