Isa ga babban shafi
Faransa

Firayi ministan Faransa, ya rufe zaman taron jam'iyar Socialist da jawabi mai karfi

A yau lahadi PM kasar Fransa Manuel Valls ya rufe zaman taron jam’iyar Socialist mai mulkin kasar Fransa a birnin La Rochelle da jawabi mai karfi na zage dantse a zabe mai zuwaShidai taron na na tsawon kwanaki uku da jam’iyar ta Socialist ta gudanar, hankalin mahalartansa ya karkata ne a kan kasassabar da ministan tattalin arzikin kasar Emmanuel Macron ya yi ne, kan awowi 36 na lokutan aiki a kasar  

Manuel Valls, na jawabi a wajen taron jam'iyar Socialis na 2015.
Manuel Valls, na jawabi a wajen taron jam'iyar Socialis na 2015. REUTERS/Stephane Mahe
Talla

A cikin jawabin rufe zaman taron Manuel Valls, ya yi kokarin saita agogan ‘yan jam’iyar ta Socialist , inda ya bukacesu, da su amince da banbance banbance dake tsakaninsu

Har ila yau Faryi Ministan Faransa, Manuel Valla ya yi fatan ganin magoya bayan jam’iyar ta yan , sun kara zage dantse wajen tunkarar zaben yankunan kasar da za a yi a cikin watan December wannan shekara ta 2015

Kusurwar da kuma yake fatan ganin magoya bayan, su tunkari, ita ce wajen yin gumurzu a zaben mai zuwa, su kuma san nauyin da ya rataya a wuyansu, tare da kara mayar da hankali da kwazo, da kuma hakkuri da juna, wanda a cewarsa sai da haka zasu iya tunkarar adawar da suke fuskanta daga jam’iyun hamayyar a kasar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.