Isa ga babban shafi

Rikici ya mamaye gasar Euro a Faransa

Rikici tsakanin magoya bayan kasashe ya mamaye kanun labaran wasannin gasar cin kofin Turai Euro 2016 da ake gudanarwa a Faransa inda a jiya sai da ‘yan sanda suka tarwatsa magoya bayan kasashen Rasha da Ingila a Lille a bata kashin da suke a saman titi.

'Yan Ingila sun yi rikici da 'Yan Rasha Lille a wasannin gasar cin kofin Turai
'Yan Ingila sun yi rikici da 'Yan Rasha Lille a wasannin gasar cin kofin Turai REUTERS/Christian Hartmann
Talla

Akalla mutane 36 ‘Yan Sanda suka kama a Lille. ‘Yan Sandan sun ce mutane 16 aka kwantar a asibiti sakamakon tashin hankali tsakanin magoya bayan Rasha da Slovakia.

Tuni dai Rasha ta kira jekadanta na Faransa domin nuna fushin kame Rashawan da Faransa ke yi a sakamakon rikicin na Euro.

Rasha ta ce kamen ‘yan kasarta ya nuna yadda ake kyamar ta, kodayake Faransa ta ce zata yi adalci wajen hukunta Rashawa da Turawan Birtaniya da aka cafke.

Wasannin Euro 2016

A yau Alhamis kuma ‘Yan Sandan Faransa sun sake damara don fuskantar karawar da za a yi yau tsakanin England da Wales.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.