Isa ga babban shafi
Faransa

Kotun Faransa ta soke wani bangare na dokar ta-baci

Kotun tsarin mulki a kasar Faransa, ta soke wani bangare na dokar ta-bacin da aka kafa a kasar domin yaki da ayyukan ta’addanci. Wannan mataki dai ya biyo bayan karar da wani ya shigar ne a gaban kotu, inda ya ke kalubalantar yadda dokar ke tauye hakkokin jama’a.

Tun a 2015 aka kafa dokar ta baci a Faransa saboda barazanar hare hare ta'addanci
Tun a 2015 aka kafa dokar ta baci a Faransa saboda barazanar hare hare ta'addanci Reuters
Talla

Wasu daga cikin bangarorin dokar da majalisar ta yi watsi da su sun hada da sashen da ke bai wa shugabannin kananan hukumomi da kantomomi damar hana shirya zanga-zangar lumana idan ana zaton cewa adadin mahalartanta zai zarta daruruwa.

Kotun tsarin mulkin ta soke bai wa shugabannin kananan hukumomin kasar damar hana wa da kuma kwace takardun da ke bai wa wasu izinin zama a yankunansu saboda dalilai na tsaro.

Hukuncin kotun dai ya biyo bayan karar da wani mutum ya shigar ne a gabanta, bayan da mahukunta a wata unguwa da ke birnin Paris suka hana shi damar ci gaba da rayuwa a inda ya ke saboda dalilai na tsaro.

A karshen shekara ta 2015 ne tsohuwar gwamnatin Francois Hollande ta kafa wannan doka lura da yadda kasar ke fama da ayyukan ta’addanci, kuma ga alama shugaba Emmanuel Macron zai bukaci majalisar dokoki ta tsawaita wa’adin aiki da ita.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.