Isa ga babban shafi
Faransa

Hollande ya bukaci kafa dokar ta baci watanni 3 a Paris

Shugaban kasar Faransa Farncois Hollande ya bukaci aiwatar da dokar ta baci na watanni uku a birnin Paris, wanda ake ganin zai kunshi ranakun gudanar da taron sauyin yanayi da za’a fara a karshen wannan watan.

Shugaban kasar Faransa François Hollande
Shugaban kasar Faransa François Hollande REUTERS
Talla

Majiya daga Majalisar kasar dake shaidawa Kamfanin dilancin Labaran faransa AFP batun, na cewa sanya wannan doka sama da kwannaki 12 na bukatar amincewar Majalisar kasar.

A yanzu dai alkallumar mamata harin Paris ya karu zuwa 132, bayan mutuwar wasu mutane 3 a yau lahadi cikin mutane sama da 350 da ke kwance a asibiti, yayin da wasu 42 yanzu haka ke cikin hali mai tsananin.

A ranar 30 ga watan Nuwamba ake saran fara taron sauyin yanayi da shugabanni duniya da dama za su hallatar a Birnin na Paris.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.