Isa ga babban shafi

Faransa ta killace wasu yankunan kasar 2 saboda korona

Shekara guda bayan killacewar farko da ta haifar da tsayawar Faransa cak, na tsawon watanni  2,  a ranar laraba 17 ga watan maris 2021, shugaba  Emmanuel Macron ya sake mutunta zabin, mai matukar wahala wajen sake killace yankunan kasar 2, dake fama da matsalar Korona. Yankunan da suka hada da Ile-de-France da Haut-de-France, duk kuwa da alkawalin da ya yi  cewa ba zai sake killace yankunan kasar ba.

shugaban Faransa Emmanuel Macron da ministan kiyon lafiyarsa  Olivier Véran, a yayin wata ziyarar da ya kai a sashen dake kulla da masu fama da tsannanin cutar Korona dake babban asibin Poissy/Saint Germain a  Laye, kusa da birnin Paris, a ranar 17 ga watan maris 2021.
shugaban Faransa Emmanuel Macron da ministan kiyon lafiyarsa Olivier Véran, a yayin wata ziyarar da ya kai a sashen dake kulla da masu fama da tsannanin cutar Korona dake babban asibin Poissy/Saint Germain a Laye, kusa da birnin Paris, a ranar 17 ga watan maris 2021. © REUTERS - POOL
Talla

’An toshe ramen Bera a Île-de-France ».  wannan Furuci ya fito ne daga bakin daya daga cikin shuwagabanin gungun masu  rinjaye a majalisar dokoki a yayin bayyana damuwarsa kan halin matsi da annobar da jefa yankunan a  ciki.

Daga cikin niyar da ya dauka, shugaba Emmanuel Macron ya ce zai bi,  duk wata hanya da ta dace wajen kaucewa sake killace yankunan kasar,  kafin zuwan lokacin da za a yi wa daukacin yankunan alurar rigakafin da zata bada damar kawar da barazanar da ake fuskanta.

Sai dai ‘yan kwanaki bayan haka,  yankin birnin  Paris mai kunshe da mutane miliyan 12 ya sake fadawa cikin danja,  al’amarin da ya tsoratar da wata minista da ta kasa shiga sashen da ke kula da tantance mutanen da suka kamu da korona a Asabiti

wasu likitoci na kokarin ceto rayuwar wani dake fama da tsananin cutar  coronavirus a asibitin  Melun-Senart dake kusa da birnin  Paris, a France, a  20, ga watan nowamba 2020. REUTERS/Benoit Tessier
wasu likitoci na kokarin ceto rayuwar wani dake fama da tsananin cutar coronavirus a asibitin Melun-Senart dake kusa da birnin Paris, a France, a 20, ga watan nowamba 2020. REUTERS/Benoit Tessier REUTERS - BENOIT TESSIER

A farkon wannan mako ne dai, shugaban Emmanuel Macron ya shanye gajearar kwana a dubu, wajen amincewa kansa cewa ya yi rauni a yaki da  annobar da ta gagari duniya, inda ya ce  babu shakka ya zama wajibi a sake kara daukar sababin matakai cikin yan kwanaki masu zuwa. Sanarwar umarnin killace yankunan dai ta  fito ne daga bakin pm kasar Jean Castex .

A yayin da shi kuma shugaba Emmanuel Macron ya sanya hannun soma aiki da dokar killacewar a ranar laraba 17 ga watan maris 2021.

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.