Isa ga babban shafi
Faransa - Afrika

Macron ya bukaci kasashe masu arziki su taimakawa Afrika da allurar rigakafin korona

Shugaban Fransa Emanuel Macron, ya shawarci kasashen masu karfin arziki da su ware kashi 3 zuwa 5 na magungunan rigakafin da su ka mallaka dan tallafawa kasashen Afrika.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron bayan tattaunawar kwamitin tsaron kasashen Faransa da Jamus ta hoton bidiyo
Shugaban Faransa Emmanuel Macron bayan tattaunawar kwamitin tsaron kasashen Faransa da Jamus ta hoton bidiyo Reuters
Talla

Wannan kira, na Shugaba Macron dai baya rasa nasaba da laakari da fadi tashin da kasashen Afrika ke yi dan ganin sun samar da maganin rigafin wa alummarsu, lamarin da yazo kwana guda kafin taron gungun kasashe 7 masu karfin arziki na duniya, a kasar Birtaniya. Ya kara da cewa, gazawa wajen aiwatar da hakan, hakika ba zai haifar da d’a mai ido ba, wa kasashen duniya.

Macron, yace Waziyariyar kasar Jamus Angela Merkel na goyon bayan kungiyar kasashen turai kuma yana fatan za’a shawo kan Amurka ma.

Sai dai kuma zuwa yanzu wasu kasashe matalauta na cikin duhu a kan cutar, a ya yin da kasashen da suka ci gaba masu karfin arziki,tuni su ka fara allurer rigakafin cutar,a cewar sa,lamarin da yace ba za’ a amince dashi ba domin hatsarinsa wa duniya.

Macron, dan shekaru 43 ya amince da tsarin China na rabawa kasashe mabukata maganin allurar rikafin da sukewa kallon kaskantar da kai ne yayin da wasu ke saya kamar Pakistan da Turkey da Hadediyar Daular Larabawa da wasu daga nahiyar Afrika.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.