Gasar cin kofin Turai da ake kira EURO, a bana ne za’a gudanar da gasar karo na 14 a hadin gwiwar kasashen Ukraine da Poland karakashin jagorancin hukumar EUFA da ke kula da kwallon kafa a Turai.
Wannan ne karo na farko da za’a fara gudanar da gasar a kasashen Ukraine da Poland bayan hukumar EUFA ta amince kasashen su dauki nauyin gasar a shekarar 2007.
A ranar 8 ga watan Juni ne za’a bude gasar inda za’a kwashe tsawon mako uku zuwa ranar 1 ga Yuli.
Kasashen 16 ne zasu fafata da suka hada da Ukraine da Poland wadanda zasu karbi bakuncin gasar.
Shirin Duniyar wasannin ya yi bayani ne game da gasar cin kofin Turai da za’a fara a ranar 8 watan Yuni ranar Juma’a mai zuwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu