Isa ga babban shafi
Afrika ta Kudu

An tuhumi Pistorius dan tseren gudun guragu da kisan Budurwar shi

‘Yan sandan kasar Afrika ta Kudu sun tuhumi dan tseren gudun guragu da laifin kisan budurwar shi a lokacin bukin ranar masoya da ake kira Valentine. Babban Jami’in ‘Yan sanda, laftanal Kanal Katlego Mogale shi ne ya tabbatar da tuhumar da suke wa dan tseren gudun guragun wanda ya karbi lambobin  yabo a wasannin Olympics da aka gudanar a birnin London.

Oscar Pistorius a hannun 'yan sandan Africa ta kudu
Oscar Pistorius a hannun 'yan sandan Africa ta kudu REUTERS/Stringer
Talla

‘Yan sanda sun ce burdurwar shi ta sha harsashen bindiga ne har sau hudu, wadda kawayenta suka kira da sunan Steenkamp.

Masu gabatar da kara a kasar Afrika ta Kudu sun dage sauraren karar Oscar Pistorius, har sai zuwa ranar Juma’a saboda za su gudanar da gwajin jini.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.