Isa ga babban shafi
FIFA

Bayern Munich ta lashe kofin Duniya a Morocco

Kungiyar Bayern Munich ta lashe kofin zakarun kungiyoyin kwallon kafa na duniya bayan ta doke kungiyar da ta wakilci Afrika Raja Casablanca ta Morroco ci 2-0. Wannan ne kofi na Biyar da Bayern Munich ta lashe a 2013 bayan lashe kofin Super na Turai da kofin zakarun Turai da Bundesliga da kofin Jamus.

'Yan wasan Bayern Munich suna murnar lashe kofin zakarun kungiyoyin duniya a kasar Morocco bayan doke Raja Casablanca a wasan karshe da aka gudanar a ranar 21 ga watan Disemba 2013
'Yan wasan Bayern Munich suna murnar lashe kofin zakarun kungiyoyin duniya a kasar Morocco bayan doke Raja Casablanca a wasan karshe da aka gudanar a ranar 21 ga watan Disemba 2013 REUTERS/Youssef Boudlal
Talla

Wannan ne kuma karo na uku da Pep Guardiola ya lashe kofin gasar bayan ya lashe kofin sau biyu a lokacin da yana Barcelona.

Wadannan kofunan da Bayern Munich ta lashe Franck Ribery yana fatar zai doke Messi da Ronaldo domin zama gwarzon duniya a bana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.