CAF
Cote d’Ivote ta amince ta buga wasa da Saliyo
Kasar Cote d’Ivoire ta amince ta buga wasa da kasar Saliyo bayan kasar tace zata kauracewa wasan saboda barazanar Ebola da ta yi kamari a kasar. Cote d’Ivoire ta amince ne ta buga wasan ne da Saliyo mai fama da Ebola don gudun kada a dauki matakin haramta mata shiga gasar cin kofin Afrika.
Wallafawa ranar:
Talla
Hukumar kwallon Cote d’Ivoire tace tuni manyan ‘Yan wasanta irinsu Yaya Toure na Manchester City da Solomon Kalou na Hertha Berlin da Gervinho na AS Roma suka isa birnin Abidjan domin fafatawa a wasan da za a buga a ranar Lahadi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu