Isa ga babban shafi
AFCON 2015

An hada Afrika ta kudu a rukuni mai zafi

An hada rukunin kasashen da zasu fafata a gasar cin kofin Afrika da za’a gudanar a kasar Equatorial Guinea, kuma a rukunin A an hada Equatorial Guinea mai masaukin baki rukuni guda da Gabon da suka taba karbar bakuncin gasar a 2012 da kuma Congo da Burkina Faso.

Taswirar Afrika dauke da tutar kasashen da za su haska a gasar cin kofin nahiyar a Equatorial Guinea
Taswirar Afrika dauke da tutar kasashen da za su haska a gasar cin kofin nahiyar a Equatorial Guinea
Talla

Rukunin B kuma an hada Zambia ne da Jamhuriyyar Congo da Cape Verde da kuma Tunisia.

Rukunin C wanda ake ganin ya fi zafi da jan hankali, an hada kasar Afrika ta kudu ne da Ghana da Senegal da kuma Algeria.

A rukunin D an hada Cote d’Ivoire ne da Guinea da Kamaru da kuma Mali

A ranar 17 ga watan Janairu ne za’a fara gasar a kammala 8 ga watan Fabrairun 2015.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.