Isa ga babban shafi
Wasanni

An yi kuskuren kora na daga aiki- Allardyce

Tsohon kocin tawagar Ingila, Sam Allardyce da aka kora a jiya Talata, ya bayyana cewa, akwai kuskure a hukuncin da hukumar kwallon kafar kasar ta dauka a kansa.

Tsohon kocin Ingila Sam Allardyce
Tsohon kocin Ingila Sam Allardyce REUTERS/Carl Recine/File Photo
Talla

Hukumar ta sauke Allardyce ne bayan ya jagoranci kasar na tsawon kwanaki 67 sakamakon katobarar da ya yi a ganawarsa da jaridar Daily Telegraph, in da bayar da shawarwari kan karya dokokin cinikayyar ‘yan wasa.

Sannan kuma ya caccaki hukumar kwallon Ingila da kuma Roy Hodson da ya gada a matsayin kocin kasar.

Sai dai Mr. Allardyce ya shaida wa manema labarai a yau cewa, tarkon da ‘yan jaridu suka nada masa ya yi nasara kuma ya amince da haka.

'Yan jaridun dai sun gabatar da kansu ga Allardyce a matsayin 'yan kasuwa, in da suka tattauna da shi kan batutuwa da dama tare da nadan kalamansa cikin sirri, yayin da kocin ya shagala tare da furta kalaman da suka kai shi suka baro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.