Wasanni
A shirye nake na sallami 'yan wasana - Ranieri
Mai horar da kungiyar Leicester City Claudio Ranieri, cikin fushi ya bayyana cewa, a shirye yake ya sallami wasu daga cikin ‘yan wasansa dan farfado da karsashin kungiyar.
Wallafawa ranar:
Talla
Tsawon wasanni 6 kenan kungiyar Leicester City na gaza samun nasara a kakar wasannin kasar Ingila ta bana, zalika suka yi rashin nasara a wasan da suka buga da Swansea City a ranar Lahadin da ta gabata.
A halin yanzu maki guda kawai ya rage Leicester City da ke rike da kofin Premier su afka cikin ajin dagaji a gasar ta kasar Ingila.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu