Kokarin Neman Na 4 A Ingila Ya Kara Zafafa
Kungiyoyin kwallon kafa a Ingila na ci gaba da fafutukar ganin sun kare a matakin da bai gaza na 4 ba domin samun damar shiga gasar cin kofin kungiyoyin zakarun nahiyar Turai a kaka mai zuwa.
Wallafawa ranar:
Gurbi 2 ne ya rage biyo bayan nasarar lashe gasar da Chelsea ta yi, inda kuma Tottenham ta samu adadin makin da ya tabbatar ma ta da gurbin shiga gasar. Yanzu dai Manchester City, Liverpool, Arsenal, da kuma Manchester United ke neman karewa a mataki na 4.
Saura wasanni biyu suka rage a gasar bayan buga wasanni 36 da akayi, Manchester City na mataki na 3 a teburin Premier da maki 72, Liverpool ta hudu da maki 70, Arsenal ta biyar da maki 69 sai kuma Manchester United ta shida ta maki 65 duk da yake ta nada kwanten wasa daya.
Chelsea ta lashe gasar ta Premier a wannan shekara bayan samun nasara akan Westbrom da ci daya da nema a ranar Juma’a da ta gabata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu