Isa ga babban shafi
Wasanni

Najeriya zata karbi bakuncin gasar kokowa ta nahiyar Africa

Najeriya ta samu nasarar zama kasar da zata karbi bakuncin gasar kokokowa ta nahiyar Africa, wadda zata gudana daga ranar 7 zuwa 11 ga watan Fabarairun shekara ta 2018, bayan da ta kada kasar Tunisia da itama ta nemi wannan dama.

Wasu mata 'yan wasan kokowa da ke wakiltar Najeriya.
Wasu mata 'yan wasan kokowa da ke wakiltar Najeriya. thenationonline.ng
Talla

Kasashen 43 ne ake sa ran zasu fafata a gasar ta kokokowa, wadda karo na farko kenan Najeriya zata karbi bakuncinta, tun bayan shekarar 1976.

Tuni dai gwamnatin Jihar Rivers da ke kudancin kasar ta bayyana cewa a shirye ta ke ta karbi wannan nauyi, na gudanar da gasar a cikinta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.