Giggs na dab da fara horar da tawagar Wales
Tsohon dan wasan Manchester United, Ryan Giggs na shirin karbar aikin horar da tawagar kwallon kafa ta Wales a kan kwantiragin shekaru hudu.
Wallafawa ranar:
Hukumar kwallon kafar Wales za ta gudanar da taron manema labarai a yammacin yau Litinin a birnin Cardiff, in da a hukumance za ta kaddamar da Giggs a matsayin sabon kocin tawagar kasar.
Tsohon dan wasan zai maye gurbin Chris Coleman wanda ya koma horar da kungiar kwallon kafa ta Sunderland a cikin watan Nuwamban bara.
Hukumar kwallon kafar kasar ta jima tana son kulla kwantiragi da Giggs don horar da ‘yan wasanta da suka gaza samun gurbi a gasar cin kofin duniya ta 2018 a Rasha.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu