Super Eagles ta lallasa Seychelles har gida da ci 3 da nema
Super Eagles ta Najeriya ta yi nasarar lallasa Pirate ta Seychelles da ci 3 da nema a wasannin neman gurbin shiga gasar cin kofin Afrika da za ta gudana a Kamaru cikin shekarar 2019.
Wallafawa ranar:
Super Eagles din ta samu kwallayenta uku ne daga Ahmed Musa da Chidozie Awaziem da kuma Odion Oghalo.
Wasan dai shi ne karon farko a tarihin tamaula da kasashen biyu suka kara da juna.
Seychelles ba ta taba samun gurbin fafatawa a gasar ta cin kofin Afrika ba, yayinda Najeriya kuma rabonta da zuwa gasar tun a shekarar 2013 bayan lashe kofin.
A bangaren guda itama Kenya ta lallasa Ghana da ci daya mai ban haushi, sai kuma Namibia da itama ta lallasa Zambia da ci da ya da nema duk dai a wasannin na neman gurbin shiga gasar cin kofin Afrika.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu