Najeriya ta tsallaka kwata final a gasar kwallon kwando ta duniya
Najeriya ta zama kasa ta farko daga nahiyar Afrika da ta samu nasarar kaiwa matakin wasan kwata final, a gasar cin kofin duniya na kwallon Kwando, ajin mata da ke gudana a kasar Spain.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
‘Yan kwallon kwandon Najeriyar, D’Tigress sun samu matakin na gaba ne, bayan samun nasara kan Girka kwallaye 57-56.
To sai dai masu iya magana sun ce wuyar aiki ba’a fara ba, domin kuwa a ranar Juma’ar nan ‘yan kwallon kwandon na Najeriya D’Tigress, za su fafata da masu rike da kofin duniyar na kwallon kwandon wato Amurka, a wasan zagayen kuda da na karshe.
A halin yanzu dai mafi akasarin masu bibiyar gasar cin kofin duniyar na kwallon kwandon, na kallon wasan na gobe da Najeriya za ta Fuskanci Amurka a matsayin mafi wahala da za ta buga a bana, la’akari da irin tarihin bajintar da Amurka ke nunawa a fagen kwallon Kwando.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu