Manchester United ta shiga tsaka mai wuya
Manchester United na fuskantar kalubalen rasa damar kaiwa zagayen kwata final a gasar cin kofin zakarun nahiyar Turai ta bana.
Wallafawa ranar:
Kalubalen ya biyo bayan rashin nasarar da suka yi a filin wasansu na Old Trafford, yayin wasan da suka fafata na ranar Talata, wanda PSG ta samu nasara da kwallaye 2-0.
PSG ta jefa duka kwallaye biyun a ragar United bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, ta hannun ‘yan wasanta Presnel Kimpembe da Kylian Mbappe.
Wani karin kalubale da United ka iya fuskanta shi ne rashin dan wasanta na tsakiya Paul Pogba a wasanta na gaba da kungiyar ta PSG, kasancewar a ba zai samu damar buga wasan ba, saboda jan katin da alkalin wasa ya bashi, bayan karbar katunan dorawa 2.
A ranar 6 da watan Maris, Manchester United za ta yi tattaki zuwa Paris don fafatawa da PSG zagaye na biyu a gasar ta zakarun Turai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu