Isa ga babban shafi
Wasanni

Najeriya ta rasa matsayi na uku a gasar cin kofin Afrika

Najeriya ta rasa damar samun matsayi na uku a gasar cin kofin nahiyar Afrika ta matasa ‘yan kasa da shekaru 20, wadda kasar Nijar ke karbar bakunci.

Tawagar kwallon kafa ta Najeriya, 'yan kasa da shekaru 20.
Tawagar kwallon kafa ta Najeriya, 'yan kasa da shekaru 20. Pulse.ng
Talla

Najeriya ta fafata wasan neman mataki na uku ne da Afrika ta Kudu, wanda ya kai ga bugun daga kai sai mai tsaron gida, bayan da suka shafe mintuna 90 da karin lokaci ba tare da kowa ya jefa kwallo a ragar dan uwansa ba.

A zagayen bugun daga kai sai mai tsaron gidan ne Afrika ta Kudu ta samu nasara kan Najeriya da kwallaye 5-3.

Duk da rashin nasarar dai Najeriya ta samu tikitin halartar gasar cin kofin duniya ajin matasa ‘yan kasa da shekaru 20 ta wannan shekara, da kasar Poland za ta karbi bakunci a watan Mayu.

Da yammacin Yau Lahadi za a buga wasan karshe tsakanin Senegal da Mali a filin wasa na Seynu Kounche da ke Yamai babban birinin Jamhuriyar Nijar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.