Isa ga babban shafi
Wasanni

Najeriya ta samu nasarar doke Masar karon farko cikin shekaru 29

Najeriya ta doke Masar da 1-0, a wasan sada zumuncn da suka buga ranar Talata, 26 ga watan Maris, a filin wasa na Stephen Keshi dake Asaba, a jihar Delta.

Mai horar da tawagar Super Eagle ta Najeriya Gernot Rohr tare da Alex Iwobi dake kungiyar Arsenal.
Mai horar da tawagar Super Eagle ta Najeriya Gernot Rohr tare da Alex Iwobi dake kungiyar Arsenal. Reuters
Talla

Sabon dan wasan tawagar kwallon kafar Najeriya ta Super Eagles Paul Onuachu ne ya jefa kwallon daya tilo a mintin farko da soma wasan.

Rabon da Najeriya ta samu nasarar doke Masar a wasan kwalon kafa tun a shekarar 1990, yayin gasar cin kofin nahiyar Afrika, hakan tasa nasarar ta jiya ke da muhimmanci ga Najeriya, duk da cewa a wasan sada zumunci ta samu.

Manyan ‘Yan wasan Masar da suka hada da Muhd Salah, Ahmed Hegazi da Elmohamady basu samu halartar wasan na jiya Talata ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.