Paris Saint Germain na take-taken dauko Pogba
Paris Saint-Germain ta fara tattaunawa da dan wasan tsakiya na Manchester United Paul Pogba don tantance ko yana da sha’awar canza sheka a wannan kaka.
Wallafawa ranar:
Ana ganin babbar kungiyar wasan kwallon kafar ta kasar Faransa na iya tayin Pogba a hukamance a cikin makonni masu zuwa, sai dai ba su kai ga yanke shawarar sayensa a wannan kaka ba, ko kuma za su bari ne zuwa shakara mai zuwa a lokacin da kwantiraginsa zai kare da United.
Kwantiragin Pogba na yanzu zai kare ne bazarar shekarar 2022, wato abin da hakan ke nufi shine yana iya tattaunawa da wata kungiya a watan Janairu a kan batun sauya sheka.
A makon da ya gabata ne jaridar Daily Mirror ta Birtaniya ta wallafa labarin da ke cewa Pogba ya yi watsi da kunshin kwantiragin da Manchester United ta mika mai na tsawaita zamansa a kungiyar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu