Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon Kafa

Salah ya shiga gaban jerin 'yan wasan Afrika da suka nuna bajinta

‘Yan wasan Afrika sun ci gaba da nuna bajinta a wasan farko na sabuwar kaka inda Mohamed Salah na Masar ya ci gaba da rike kambunsa a matsayin jagora a tsakaninsu bayan kafa tarihin zama dan wasan firimiya da ya zura kwallo a wasan farko na kowacce sabuwar kaka cikin shekaru 5 a jere bayan kwallonsa a karawar Liverpool da Norwich da aka tashi wasa 3 da nema.

Dan wasan gaba na Liverpool Mohammed Salah dan Masar.
Dan wasan gaba na Liverpool Mohammed Salah dan Masar. MIGUEL MEDINA AFP
Talla

Sauran ‘yan wasan da suka nuna bajinta a wasan farko na Firimiyar sun hada da Isma’il Sarr na Senegal da ke taka leda a Watford wanda shima ya zura kwallo a wasan da suka yi nasara kan Aston Villa da kwallaye 3 da 2.

Haka zalika akwai Said Benrahma na West Ham wanda shima ya taimakawa kungiyarsa nasara kan Newcastle da kwallaye 4 da 2.

Sauran ‘yan wasan Afrika da suka nuna bajinta a karshen makon sun hada da Yousef en Nasriy na Morocco da ke taka leda da Sevilla karkashin gasar Laliga sai Oussama Idriss shima dai dan Maroccon a Sevilla wadanda dukkaninsu suka yi rawar gani a wasan na jiya.

Akwai kuma Taiwo Awoniyi dan Najeriya da ke taka leda a Union Berlin karkashin gasar Bundesliga wanda shima ya zura kwallo guda a wasan da suka tashi kunnen doki da Bayer Leverkusen.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.