Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon Kafa

Marseille na daf da samun gurbi a gasar zakarun Turai

 Marseille ta koma matsayi na 2 a gasar Ligue 1 a jiya Lahadi bayan da ta lallasa Lorient da ci 3-1, lamarin da ya saka ta turbar gasar zakarun nahiyar Turai a kaka mai zuwa.

Wasu 'yan wasan Marseille
Wasu 'yan wasan Marseille Boris HORVAT / AFP
Talla

Yaran Jorge Sampaoli sun gaza shiga matakin wasan karshe na gasar nahiyar Turai ta Conference League a ranar Alhamis, sakamakon taka musu birki da  Feyenoord suka yi, amma sai gashi yanzu su na hanyar shiga babbr gasar Turai ki tsaye.

Kwallaye daga  Bamba Dieng, Matteo Guendouzi da Gerson ne suka bai wa Marseille wannan nasara mai matukar mahimanci da suka samu.

PSG, wadanda suka riga suka lashe gasar Ligue 1 ta Faransa, sun buda canjaras 2-2 da Troyes, wadanda su ma malakin kamfaanin nan na Abu Dhabi ne kamar Manchester City.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.