Isa ga babban shafi

Al'ummar Morocco sun tarbi tawagar kasar da ta nuna bajinta a Qatar

Dubun dubatan ‘yan Morocco ne suka fito a babban birnin kasar jiya Talata don tarbara tawagar kwallon kafar kasar da ta isa gida bayan ta taka rawar gaban hantsi a gasar cin kofin duniya da ta gudana a Qatar, inda ta kasance kasar Larabawa ta farko ko Afrika ta farko da ta kai matakin wasan kusa da na karshe a tarihin gasar.

Tawagar Morocco lokacin da suke zagayawa a cikin kasar.
Tawagar Morocco lokacin da suke zagayawa a cikin kasar. © Mosa'ab Elshamy / AP
Talla

‘Yan wasan tawagar a karkashin jagorancin mai horar da su Walid Regragui sun yi ta daga wa jama’a hannu daga budaddiyar motar bas din da ta dauki su ta na zagayawa da su birnin Rabat, bayan da suka baro filin jirgin saman kasar.

Dimbim ‘ya sanda ne, wasu a motoci, wasu a Babura suka yi wa ‘yan wasan rakiya, inda aka saka jiniya tare da kunna fitilu masu haske.

Taron jama’ar sun yi  ta jinjina suna daga hannuwa tare da wasa da tirtsitsin wuta.

Wasu da aka gana da su dai sun bayyana fatan cewa tawagar za ta lashe kofin duniya nan gaba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.