Isa ga babban shafi

PSG za ta biya Mbappe euro miliyan 60 a matsayin tukwicin biyayya

Rahotanni daga birnin Paris na cewa akwai yiwuwar PSG za ta biya dan wasanta Kylian Mbappe kudaden da yawansu ya kai euro miliyan 60 a matsayin tukwicin yabawa da biyayya ko amintakar da ke tsakaninsu.

Kylian Mbappé
Kylian Mbappé © FRANCK FIFE / AFP
Talla

Bayanan sun ce kungiyar ta París Saint Germaine za ta biya tauraron na ta makudan kudaden ne, muddin bai raba gari da ita har zuwa ranar 1 ga watan Agusta, duk da cewar dangantakar da ke tsakaninsu ta yi rauni matuka, biyo bayan kin tsawaita yarjejeniyarsa da yayi da ke shirin karewa a 2024.

Yanzu haka dai kungiyoyi da dama ne ke neman kulla yarjejeniya da dan wasan na Faransa.

Tuni kuma kungiyar Al-Hilal ta Saudiya ta gabatar da tayin euro miliyan 300 wanda PSG ta karba.

Sai dai Mbappe ya dage kan cigaba da zama a kungiyar ta sa, har zuwa lokacin da yarjejeniyarsa za ta kare.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.