Isa ga babban shafi
ICC-Congo-Rwanda

Za a mika Ntaganda ga Kotun Hague a wannan makon

Mai Gabatar da kara na kotun hukunta manyan laifufuka, Fatou Bensouda, ta ce a cikin wannan mako ake sa ran kai Janar Bosco Ntaganda, shugaban ‘Yan tawayen Jamhuriyar Demokradiyar Congo birnin Haque, dan fuskantar shari’a.  

Janar Bosco Ntaganda, Kwamandan 'Yan tawayen Congo
Janar Bosco Ntaganda, Kwamandan 'Yan tawayen Congo REUTERS/Paul Harera
Talla

Idan dai ba’a manta ba, Janar Ntaganda ya mika kansa ga Ofishin Jakadancin Amurka a Rwanda, kuma yana daga cikin wadanda kotun ke nema ruwa a jallo, saboda zargin kashe jama’a da kuma sanya yara kanana cikin yaki.

A yanzu haka kasar ta Rwanda na ta nisanta kanta da Ntaganda inda Ministan Shari’ar kasar, Tharsis Karugarama, ya ce bazai yin magani da yawun Ntaganda ba, sai y ace ya kamata a bashi dama ya kare kansa bisa zargin da ake yi mai.

“Ba zan iya magana da yawun Janar Ntaganda ba, ya yi zabi, shi Janar ne na sojin Congo a baya, ya zabi mika kansa dan kai shi kotun duniya, saboda haka ya dace a bashi dama dan fuskantar kotun domin kare kansa.” Inji Minista Karugarama.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.