Bankwana daga Shugaban Faransa a taron Mali
Shugaban Faransa Francois Hollande a jawabin taron Bamako da ya hada kasashen Afrika da Faransa ya gabatar da shawarwari tareda yi bankwana ga shugabanin da suka halarci taron ,inda yake fatar ganin kasashen Afrika sun shiga sahun yankunan da ake gudanar da sahihin zabe bisa tafarkin Demokradiyya.
Wallafawa ranar:
zababben shugaban kasar Gambia Adama Barrow ya gana da shugabanni da ke halartar taron kasashen Afrika da Faransa a birnin Bamako na Mali,
Wasu rahotani daga jami’an diflomasiya sun tabbatar da cewa kasashen Najeriya da Morroko sun sanar da baiwa Shugaba Jammeh Mafaka mudin ya amince sauka dama mika karagar mulki zuwa Abama Barro ranar 19 ga wannan wata da muke ciki.
Akala yan sanda dubu 10 suka tabbatar da tsaro a harabar zauren taro dama wasu muhiman wuraren babban birnin kasar Mali.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu