Isa ga babban shafi
Iraqi

Dakarun Iraki sun kama garuruwa a yankin kirkuk mai neman ballewa...

Dakarun Iraki sun karbe ikon wasu kauyuka daga hanun kurdawa a yankin Kirkuk, bayan tafka wani gumurzu da suka yi, a yayin da Amruka ta yi kiran a maida wukaikai kube.

Wata tawagar sojoji kurdawa a kusa da  da garin Altun Kurpi, 20 oktoba 2017.
Wata tawagar sojoji kurdawa a kusa da da garin Altun Kurpi, 20 oktoba 2017. REUTERS/Azad Lashkari
Talla

Rahotanni sun ce, dakarun rundunar hadaka ta JOC da ta hada daukacin jami’an tsaron Iraki ne, a jiya juma’a ta sanar da kwace garin 'Altun Kupri", da ya hada kauyuka 36 a maraba’in Km 530 inda kimanin kabilun Kurdawa da Turkmen dubu 56 ke rayuwa

Kasar Amruka ta bayyana damuwarta da sabon tashin hankalin dake faruwa a arewacin kasar ta Iraki. Kafin ta bukaci Sojan Iraki su takaita kai kawonsu a yankin na Kirkuk

Wannan sabon tashin hankali dai na zuwa ne kasa da wata guda bayan kada kuri’ar tabbatar da samun cikaken yanci cin gashin kan yankin kurdawan daga kasar ta Iraki

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.