Zimbabwe-Bankin Duniya-Najeriya
Mugabe ya soki kasashen Duniya game da shugabancin Bankin Duniya
Shugaban Kasar Zimbabwe, Robert Mugabe, ya yi mummunar suka kan matsayin da kasashen yammacin duniya suka dauka, wajen hana Ministan kudin Najeriya, Ngozi Okonjo Iweala mukamin shugaban Bankin Duniya.
Wallafawa ranar:
Talla
Mugabe yace Afrika ta yi bakin-cikin rashin samun Mukamin shugabancin Babban bankin a lokacin da ya ke shaidawa wani taron mata a Harare, wanda Ngozi Okonjo Iweala ke halarta.
Shugaban yace, babu Dan Afrika da zai shugabanci Bankin Duniya da Hukumar Bada Lamuni ta Duniya, abinda ke dada nuna rashin daidaito a tsakanin kasashen duniya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu