Isa ga babban shafi
Kenya

An samu wasu kaburbura a kasar Kenya

‘Yan Sanda a kasar Kenya, sun ce sun gano wasu kaburbura guda biyu, da aka birne mutane da dama, wadanda aka kashe a rikicin kabilancin Yankin Tana Delta. A cewar ‘Yan Sandan, suna bukatar kotu ta bada umurnin damar hako gawawakin domin gudanar da bincike akai.  

Yankin Tana da ake yawan rikici tsakanin 'Yan kabilar Pokomo da Orma
Yankin Tana da ake yawan rikici tsakanin 'Yan kabilar Pokomo da Orma Photo AFP/Simon Maina
Talla

Akalla mutane 100 aka kashe a rikicin kabilancin da aka kwashe wata guda ana yi a yankin, wanda ya lakume kujerar Ministan kasar.

“Mun gano kaburburan, kuma muna kyautata zaton za a samu wasu da dama, amma bam u san ko su wanene aka binne ba, amma ga dukkan alamu, za a samu karuwan yawan mutanen da su ka mutu a fadan fiye da yadda mu ke tsammani”, inji wani Dan sanda.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.