Isa ga babban shafi
malawi

Shugabar kasar Malawi ta yadda a rage mata albashi da kashi 30

Shugaban kasar Malawi, Joyce Banda, ta ce ta yadda da a rage kashi 30 daga cikin albashinta, a matasyin wani mataki na rage yawan kudaden da ake kashewa a kasar. Haka kuma ragin albashin zai shafi Mataimakin shugabar kasar ta Malawi, Khumbo Kachali.  

Shugaban kasar Malawi Joyce Banda
Shugaban kasar Malawi Joyce Banda Reuters / Lefteris Pitarakis
Talla

“Saboda mu nuna goyon bayanmu da matakan tsuke aljihun kasarmu, shugaban kasa da mataimakin shugaban kasa sun yadda a rage musu albashinsu da kashi 30,” inji Kachali.

Shugabar kasar dai na karban akalla Dalar Amurka 5,000 a duk wata amma yanzu za ta dinga karban Dalar Amurka 3,500 ne, a yayin da mataimakinta zai dinga karban Dalar Amurka 2,800 a maimakon Dalar Amurka 4,000.

Tun hawanta kan karagar mulki, a watan Aprilu, Banda na ta daukan matakan ganin cewa ta magance matsalolin da ke addabar tattalin arzikin kasar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.