Masar
An saka ranar sake yiwa Hosni Mubarak sabuwar shari’a
Hukumomin Kasar Masar sun ce za’a sake yiwa Tsohon shugaban kasar, Hosni Mubarak shari’a daga ranar 13 ga watan gobe, saboda zargin da ake masa na hannu wajen kashe masu zanga zanga.
Wallafawa ranar:
Talla
Wata kotun daukaka kara ta soke daurin rai da ran da aka masa, ta kuma bada umurnin sake shari’ar ta sa, tare da wasu jami’ansa, da suka hada da tsohon ministan cikin gida, Habib al-Adly da wasu manyan jami’an tsaro shida.
An dai yankewa Mubarak da Adly hukuncin kisa ne a ranar 2 ga watan Yunin bara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu