Isa ga babban shafi
Masar

Kotun Masar ta dakatar da shari’ar Morsi

Kotun kasar Masar ta dakatar da Shari’ar da ake yi wa Mohammed Morsi bayan Lauyan da ke kare tsohon shugaban da ake tuhuma da laifin bayar da umurnin kisan masu zanga-zanga ya nemi a canza alkali.

Magoya bayan Morsi na jama'iyyar 'yan uwa Musulmi ta kasar Masar
Magoya bayan Morsi na jama'iyyar 'yan uwa Musulmi ta kasar Masar REUTERS/Amr Abdallah Dalsh
Talla

Morsi shugaban mulkin dimokuradiya na farko a Masar yana fuskantar shari’a ne tun lokacin da aka tumbuke shi daga madafan ikon Masar akan zargin ya bayar da umurnin kisan masu zanga-zangar kin jinin shi a watan Disemba na 2012.

Lauyan da ke kare tsohon shugaban ya bukaci a canza biyu daga cikin Alkalan da ke Shira’ar, yana mai zargin daya daga cikinsu ya tattauna da ‘Yan jarida game da Shari’ar.

Babu tabbas dai ko Kotun kasar zata amince da bukatar Lauyan, kodayake ana saran Kotun kolin zata yanke hukunci a ranar 9 ga watan Afrilu.

Akwai zarge-zarge da dama ake tuhumar Mohammed Morsi da suka hada da batun ballewar ‘Yan gidan yari a lokacin zanga-zangar adawa da gwamnatin Hosni Mubarak a 2011.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.