Isa ga babban shafi
Angola

Mamata sun karu a ambaliyar Ruwan Angola

Mutane 64 ne aka tabbatar sun mutu sakamakon ambaliyar Ruwa da ta samo asali daga Ruwan sama masu matsanancin karfi da aka shatata a yankin yammacin kasar Angola

Lobito debaixo das intempéries
Lobito debaixo das intempéries Pedro Parente /ANGOP
Talla

Asarin wadanda suka mutu dai an same su ne a birnin Lobito da ke a gabar Ruwan Lardin Benguela, daga cikinsu kuma, akwai yara kanana 35.

Ambaliyar Ruwan kuma ta zo wa mutanen ne suna bacci da tsakiyar Dare, kuma Ruwan da aka yi da karfin gaske ya lalata gidaje da dama, abinda aka ce shi ne musabbabin mutuwar mutane da dama.

Shugaban kasar ta Angola Jose Eduardo dos Santo, ya yi alwashin taimakawa mutanen da hatsarin ya shafa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.