Isa ga babban shafi
MDD-UNHCR

20 ga watan Yuni ranar yan gudun hijira a Duniya

A yau assabar 20 ga watan Yuni, Majalisar Dimkin Duniya ta ware a matsayin ranar ‘Yan gudun hijira ta duniya, ranar da kan mayar da hankali a kan yadda za a iya inganta rayuwar miliyoyin mutane da ake musgunawa, tashin hankali, yaki da kuma cin zarafin Bil Adama ya tilastawa tserewa daga gidajen su.

Wani sassanin yan gudun hijira na yan kasar Mali a Burkina Faso
Wani sassanin yan gudun hijira na yan kasar Mali a Burkina Faso Tribouillard / AFP
Talla

Ranar a bana na zuwa ne, a daidai lokacin da Hukumar Kula da Yan gudun hijira ke cewa akalla mutane miliyan 60 ne ke gudun hijira sakamakon tashe tahsen hankulan da aka samu a shekarar 2014, wanda hakan ya nuna karuwar kusan miliyan 8 da rabi kan na shekarar 2013, kuma sama da rabin mutanen yara ne kanana.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.