Isa ga babban shafi
Kenya-Amurka

shugaba Obama na shirin soma ziyarar aiki a kasar Kenya

Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta ya sanar cewa ziyarar da shugaba Barack Obama zai kai a kasar ta kenya a ranar juma’a mai zuwa mai matukar mahinmancin ne kwarai, inda ya yi watsi da batun auren jinsi guda daga cikin batutuwan da zasu tattauna.

Barack Obama a ziyararsa a kasar Kenya a shekara ta 2006
Barack Obama a ziyararsa a kasar Kenya a shekara ta 2006 AFP PHOTO/SIMON MAINA
Talla

Shugaban kasar ta kenya Uhuru Kenyatta yace babu batun kare hakkin masu auren jinsi guda, a cikin abubuwan da za su a tattauna da shugaba Obama.

Shugaban yace Kenya, da ma Nahiyar Africa nada batutuwa masu muhimmanci dake bukatar a baiwa mahinmanci a tattauna da hukumomin Amurka, da suka kunshi sauran kasar da suke hulda da ita.

Kenyatta ya kuma yi karin haske a kan batun mataimakinsa William Ruto, da kotun hukunta manyan laifufuka ta duniya ICC ke tuhuma bisa zargin tayar da rikici bayan zabe a shekara ta 2007, kuma shi ma zai gana da shugaban na Amurka a yayin wannan ziyarar.

Kasar kenya dai ita ce asalin mahaifin shugaban na Amurka Barack Obama.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.