Rwanda
Rwanda za ta kada kuri'ar sauya kundinta
Yau ake sa ran Majalisar kasar Rwanda za ta kada kuri’ar amince wa da sauya kundin tsarin mulki domin bai wa shugaba Paul Kagame damar sake tsaya wa takara a karo na uku.
Wallafawa ranar:
Talla
Majalisar ta tafka mahawara a jiya Laraba sakamakon kudirin da magoya bayan shugaban sama da miliyan uku da rabi su ka gabatar, inda su ka bukaci sauyin saboda abinda su ka kira irin ayyukan ci gaba da shugaban ke yi wa kasar.
Idan Majalisar ta amince da kudirin za a bai wa al’ummar kasar damar jefa kuri’a a zaben raba gardama.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu