Isa ga babban shafi
Libya

An bukaci bangarorin Libya su sasanta

Wakilan Manyan kasashen Duniya masu karfi da kuma wakilan kasashen Larabawa sun bukaci bangarorin da ke rikici a kasar Libya su rungumi tayin zaman lafiya da Majalisar Dinkin Duniya ta tsara don samar da Gwamnatin hadaka.

Tun kawar da gwamnatin Marigayi Kanal Gaddafi Libya ta fada cikin rikici
Tun kawar da gwamnatin Marigayi Kanal Gaddafi Libya ta fada cikin rikici REUTERS/Esam Omran Al-Fetori/Files
Talla

Sakataren waje na kasar Amurka John Kerry na daga cikin Ministocin kasashe 20 da suka halarci taron da aka yi a Rome domin tattauna rikicin kasar Syria, inda aka gaza samun zaman lafiya tun bayan kawar da Shugaba Muammar Gaddafi a shekara ta 2011.

Kerry ya fadi cewa rikicin kasar Libya ya dauki lokaci sosai, kuma burin manyan kasashen duniya ne na ganin an sami zaman lafiya mai dorewa a kasar.

Yace hakkin manyan kasashen duniya ne su ga lallai zaman lafiya ya dawo a Libya.

Wasu jami’an kasar Libya 15 da ke wakiltan sassa daban-daban suka shiga tattaunawar zaman lafiyan.

Wakilan kasar Libyan sun kushi wakilan majalisar kasar da ke da mazauni a Tripoli da kuma wakilan wata majalisar da ke da mazauni a Tobruk, kuma dukkan su sun amince su rattaba hannu cikin yarjejeniyar zaman lafiyan ranar Laraba a Morocco.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.