Isa ga babban shafi
Rwanda-Amurka

Kagame ya yi watsi da furunci Amurka kan takararsa

Shugaban Rwanda Paul Kagame ya yi watsi da sukar da kasar Amurka ta yi masa, bayan da ya sanar da aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasar karo na uku.

Shugaban kasar Rwanda Paul Kagame
Shugaban kasar Rwanda Paul Kagame REUTERS/Ruben Sprich
Talla

Kagame wanda ke mayar da martani a shafinsa na Twitter, ya ce furucin da ma’aikatar wajen Amurka ta fitar dangane da tsayawarsa takara, kalamai ne da aka taba jin irinsu sau da dama, kuma ba za su taba magance matsalar Nahiyar Afirka ba.

Amurka dai na gani cewa tsayawar takarar Kagame a wa’adi na uku kuskure ne da zai karya lagon demokradiyar kasar, domin salon mulkin kama karya yake shirin aiwatarwa a kasar, musamman lura da yadda jam’iyyun adawa kasar ba sa wani tasiri.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.