Isa ga babban shafi
Nijar

An saki Hama Amadou jagoran adawa a Nijar

Kotun daukaka kara a Nijar ta bayar da belin Hama Amadou jagoran adawa da aka garzaya da shi asibitinin Faransa daga gidan kaso kan tuhumarsa da fataucin ‘yaya daga Najeriya, wannan na zuwa ne bayan kammala zaben shugaban kasa da Issoufou Mahamadou ya lashe.

Hama Amadou madugun adawa a Nijar
Hama Amadou madugun adawa a Nijar ISSOUF SANOGO / AFP
Talla

Kotun ta bayar da umurnin sakin Hama a yau Talata, kamar yadda Lauyan da ke kare shi Mossa Boubakar ya tabbatar.

Tun a ranar 16 ga watan Maris ne aka garzaya da Hama zuwa Asibitin Faransa daga gidan kaso a yayin da ya rage kwanaki a gudanar da zabe zagaye na biyu tsakanin shi da Shugaba mai ci Mahamadou Issoufou.

‘Yan adawa sun kauracewa zaben saboda rashin sakin Hama, tare da yin watsi da sakamakon zaben da Issoufou ya lashe da sama da kashi 92.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.