Mutane 3 sun mutu a harin bam a Somalia
Bam da aka dasa a cikin mota daf da gidan sayar da abinci a yau asabar, ya fashe tare da hallaka mutane 3 da kuma jikata wasu biyar a tsakiyar kasar ta Somaliya, an tabbatar da cewa dukkan mutanen da al’amarin ya shafa fararen hula ne.
Wallafawa ranar:
Kakakin karamar hukumar yankin birnin Mogadishu Abdifatah Oumar ne ya shedawa manema labarai yadda al’amarin ya auku da kuma yawan mutanen da suka rasa rayukansu.
Sai dai Oumar yace zai yi wuya a san ko su waye suka kai wannan harin a yanzu duk da cewa hare-hare irin wannan baya rasa nasaba da ayyukan kungiyar Alqaida ko El-shabab dake ci gaba da tayar da kayar baya a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu