Isa ga babban shafi
Najeriya

Makarantar Horar da Sojoji na musamman ta koma Buni Yadi

Rundunar Sojin Najeriya ta mayar da cibiyar horar da sojoji na musamman zuwa garin Buni Yadi na Jihar Yobe, wanda Mayakan Boko haram suka taba kwacewa.

Janar Tukur Buratai
Janar Tukur Buratai AFP PHOTO/STRINGER
Talla

An dauke makarantar ne daga Jihar Niger kuma babban hafsan sojin Kasar Janar Tukur Buratai ya ce saboda fada da Boko Haram aka dawo da makarantar zuwa Buni Yadi.

Janar Buratai ya ce Buni Yadi ya kasance hanyar da mayakan na Boko Haram ke bi zuwa sassan yankin arewa maso gabashi har zuwa Jihar Filato.

An kirkiro Makarantar ne ta horon sojoji na musamman a lokacin da sojojin Najeriya ke fada gadan-gadan da Mayakan Boko Haram

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.