ECOWAS ta soke ziyara a Gambia
Shugabannin Kasashen Yammacin Afrika sun soke kai ziyara a wannan Laraba a kasar Gambia a kokarin shawon kan Yahya Jammeh don ganin ya mika ragamar mulki ga Adama Barrow, in da aka dage kai ziyarar har zuwa ranar juma’a mai zuwa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Garba Shehu, mai magana da yawun shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce, duk da cewa an dage ganawar da aka tsara yi a yau laraba, amma fa matsayin shugabannin kasashen yankin na ganin cewa Jammeh ya mika ragamar mulki a karshen wa’adinsa na nan daram.
Wannan kuma na zuwa ne a wani lokaci da babban mai sharia na kasar Emmanuel Fagbenla ya sanar cewa, a cikin watan biyar ko na sha-daya za su saurari batun makudi da Yahya Jammeh ya ce an yi a zaben.
A farko dai shugaba Jammeh da ya mulki Gambia na tsawon shekaru 22 ya amince da shan kayi a zaben na watan jiya, amma daga bisani ya tubure bayan ya zargi jami'an hukumar zaben kasar da tafka kura-kurai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu