Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

Amurka na son a kakabawa Sudan ta Kudu takunkumin sayan makamai

Kasar Amurka ta sake rokon kwamitin Sulhu na Majalisar dinkin Duniya da ya sake nazari kan muhimmanci sanyawa kasar Sudan ta kudu takunkumin sayen makamai saboda yadda al’amura ke ci gaba da tabarbarewa a kasar.

'Yan gudun hijirar kasar Sudan ta kudu  yayinda suke dakon a yi musu rijistar karbar abinci da hukumar kula da samar da abinci ta majalisar dinkin duniya  (WFP) ke rabawa a yankin Thonyor, a jihar Leer state, da ke Sudan ta Kudu.
'Yan gudun hijirar kasar Sudan ta kudu yayinda suke dakon a yi musu rijistar karbar abinci da hukumar kula da samar da abinci ta majalisar dinkin duniya (WFP) ke rabawa a yankin Thonyor, a jihar Leer state, da ke Sudan ta Kudu. REUTERS/Siegfried Modola
Talla

Jakadiyar Amurka a kwamitin Nikki Haley tace bukatar Majalisar na tsagaita wuta da baiwa jami’an agaji damar gudanar da ayyukan su da kuma tattaunawa dan warware rikicin kasar sun ci tura.

Zalika Haley ta zargi gwamnatin shugaban Sudan ta Kudun Salva Kiir da kirkirar yunwa a kasar sakamakon gaza aiwatatr da yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma da ‘yan tawayen kasar, wanda daga ciki shi ne janye sojin kasar daga tituna zuwa barikokinsu.

Kasashen Faransa da Birtaniya sun goyi bayan matsayin na Amurka amma Rasha da China sun hau kujerar na ki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.