Kungiyar Tarayyar Africa Ta Ja Kunnin Kasashen Djibouti da Eritrea
Kungiyar Tarayyar Africa ta roki kasashen Djibouti da Eritria da su rungumi tattaunawan zaman lafiya maimakon kai ruwa rana a rikin da ya sarke tsakaninsu saboda batun kan iyaka.
Wallafawa ranar:
A jiya Juma’a Ministan waje na kasar Djibouti Mahamoud Ali Youssouf ke zargin Eritria da cewa ta mamaye tsaunukan Dumeira inda suke takaddamar sa.
A baya an jibge sojan wanzar da zaman lafiya na kasar Qatar a kan iyakan kasashen biyu, amma kuma tun da sojan suka janye ne aka fara samun sabuwar takaddamar.
A sanarwar da Kungiyar Tarayyar Turai ta fitar yau Asabar, da sa hannun Moussa Faki Mahamat na cewa kasashen biyu su kiyaye da ga tada husuma.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu