Somalia
Sojin Amurka sun kai sabbin hare-hare kan Al-Shabaab
Kasar Amurka ta kaddamar da sabbin hare-hare kan mayakan Al-Shabab a kasar Somalia, shi ne karo na biyu cikin wannan wata an Yuli.
Wallafawa ranar:
Talla
Mai magana da yawun sojin Amurka dake kula da nahiyar Africa Patrik Barnes, ya ce nan gaba kadan zasu bayyana irin nasarorin da suka samu a harin da suka kai wa mayakan Al-Shabaab.
A cewar Barnes, burin Amurka shi ne taimakawa Somalia domin murkushe ‘yan kungiyar Al-Shabab don kasar ta sami kwanciyar hankali.
Tun a shekara ta 2007 Al-Shabaab da ke alaka da Al-Qa’eda ke fafutukar ganin ta hambarar da gwamnatin Somalia.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu