Isa ga babban shafi
Najeriya

Boko Haram ta kashe ‘Yan kato da gora 680 a shekaru uku

Kungiyar matasan da ke taimakawa sojojin Najeriya wajen yaki da Boko Haram da ake kira Civilian JTF ko kuma kato da gora, tace akalla mambobinta 680 aka kashe a cikin shekaru 3 da suka gabata a Jihar Borno.

'Yan kato da Gora da dama ne suka ji rauni a fada da Boko Haram
'Yan kato da Gora da dama ne suka ji rauni a fada da Boko Haram REUTERS/Akintunde Akinleye
Talla

Mai ba kungiyar shawara kan harkokin shari’a Jubril Gunda wanda ya bayyana wadanda aka kashe a matsayin gwarzaye ya ce sun mutu ne sakamakon hare hare daban daban da kungiyar Boko Haram ta kaddamar a sassan jihar Borno.

Gunda wanda ya yabawa Gwamnatin Jihar Barno da ke tallafa wa ‘Yan kato da gora wajen gudanar da ayyukansu, ya kuma bukaci gwamnatin Najeriya ta tallafawa iyalan wadanda aka kashe domin samun sanyi a rayuwarsu.

A 2014 ne matasan suka shiga yaki da Boko Haram tare da samun goyon baya daga rundunar sojin Najeriya da kuma samun tallafi daga gwamnatin Jihar Borno.

Boko Haram ta salwantar da rayukan dubun dubatar mutane tare da raba miliyoya da gidajensu a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.