'Yan Bindiga Sun Kai Hari Gidan Mataimakin Shugaban Kasar Kenya William Ruto
A kasar Kenya wasu ‘yan bindiga sun kai hari gidan Mukaddashin Shugaban kasar William Ruto yau Asabar, makonni kasa da biyu kafin babban zaben kasar mai cike da rudani.
Wallafawa ranar:
Majiyoyin samun labarai sun shaidawa kamfanin Dillancin labaran Faransa AFP cewa an kai wannan hari ne a lokacin da Mukaddashin Shugaban kasar ba ya cikin gidan, kuma har an jikkata wani jami’in tsaro mai gadi.
Wani jami’in Gwamnati ya gaskata cewa an kara jibge jami’an tsaro a gidan Mukaddashin Shugaban sannan kuma ana ci gaba da gudanar da binciken lamarin.
Shugaba Uhuru Kenyata wanda William Ruto ke yi wa mataimaki za su sake fafatawa ne a babban zaben kasar ranar takwas ga watan gobe da tsohon dan adawa Raila Odinga.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu